Credits
COMPOSITION & LYRICS
Nazifi Asnanic
Songwriter
Lyrics
Dan marayan zaki, Allah ke baka abinci
Dan marayan zaki, rike ma'aiki ka wuce kunci
Dan marayan zaki, yi alwala kaje masallaci
Dan marayan zaki, kar kaiwa kowa habaici
Dan marayan zaki, waka batasa kai takaici
Dan marayan zaki, kai waka kurum da azanci
Dan marayan zaki, magana karta hana kayi barci
Dan marayan zaki, ga albishir ban tukuici
Dan marayan zaki, kara rike Allah a zuci
Zauna da lafiya da kowa da wata rana kana makwanci
Yiyah, ni na gode sarki Allah bani dogaro a kan kowa ba
Kuma na gode sarki Allah ban iya in yaudara ko daya ba
Allahu ni ina gode ma ba'a sanni fagen cuta ba
Allahu na godema ka ban basira ban raina ba
Allahu kai ka amince inyi waka ko ban kyama ba
Allah da yardarka munkaje Madina ziyara babba
Allah da yardarka anka ganmu koda mutum bai so ba
Allahu yanda kaso kakayi ka dauken uwa ban so ba
Allahu na godema kyautarda kayine ba wani ba
Mahmudu ka bani Muhammadu, sai gasu ban auneba
Allahu sa musu soyayyar ma'aiki rabasu da kunci
Dan marayan zaki, kara rike Allah a zuci
Zauna da lafiya da kowa dun wata rana kana makwanci
Eyy ban kida zanyi waka ban zo in zagi dan kowa ba
Kaban kida kurum waka zan kai daga jinka ba shirmeba
Taken ta in kaji wakar ka san banyo shirin wasa ba
Ban danyo zubin wasa ba sannan banyo shirin roko ba
Idan kaji tai maka zafi wallahi ba nufi na kai ba
Wakar kawai nake waka kuma ba gadona ba
Iyakaci in fadi abunda na sani don bazan boye ba
Inma ka zageni kaje ka zagi ba zaya fito ba
Inma ka cuce ni to cutarka batayi rana ba
Da ace wanine ke badawa sai mu rasa abinci
Dan marayan zaki, kai waka kurum da azanci
Kai mai talla ka dau tallakka wata rana kamar ba kai ba
Karka hangi wanda ya fika kace zaka gunsa ba dai-dai ba
Rayuwa irin ta duniya wani ya fika wanin bai kai ba
Kar kayi gaggawa domin bukata ba zata biya ba
Gaggawa aikin shedan haka naji ba ni na fada ba
Tsaya matsayinka yaro duniya ba gida na zama ba
Ka lura da me kakeyi Allah sa ba haramunne ba
Da akwai wata magana da zana barta ban tono ba
Kar kai zatonma da kai nake zancenga ni na saba
Zana furta zancen domin bam son barinsa a zuciya
Dan marayan zaki, yi alwala kaje masallaci
Dan marayan zaki, Kar kayiwa kowa habaici
Ban niyyar ince komai ba ba kuma don ina tsoro ba
Naso in bar kaza a cikin gashin ta ban figa ba
Amma na lura wadansu na batu basu san kara ba
Wanzami bai son jarfa shi bai so a maida mai ba
Matsala ta baki sai ya fada harshen sa bai tauna ba
Da an mai da mai sai yaji da tun fari bai furucin ba
Da zan bude zancen nan matsayin ka ba zai wuce jaki ba
Da zana baje maganar idon kowa ba bakafi kare ba
Inda zana tone ko a gidanka baka yi min gurni ba
Riga ta mutunci ita nasa in banda hakan da kace
Dan marayan zaki, Allah ke baka abinci
Dan marayan zaki, rike ma'aiki ka wuce kunci
Dan marayan zaki, yi alwala kaje masallaci
Dan marayan zaki, kar kaiwa kowa habaici
Dan marayan zaki, waka batasa kai takaici
Dan marayan zaki, kai waka kurum da azanci
Dan marayan zaki, magana karta hana kayi barci
Dan marayan zaki, ga albishir ban tukuici
Dan marayan zaki, kara rike Allah a zuci
Zauna da lafiya da kowa da wata rana kana makwanci
Lyrics powered by www.musixmatch.com